Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin Arab Alyaum cewa, Fahad Affasi minister mai kula davharkokin addini na Kuwait, da kuma Ahmad Azum ministan ma’aikatar kula da harkokin addini Tunisia sun rattaba hannu kan yarjejeniyar da ta shafi ayyukan kur’ani.
Bayanin ya ce an rattaba hannu kan wannan yarjjeniya nea kasar Tunisia a ziyarar da ministan na Kuwait ya kai kasar, inda suka cimma matsaya kan yin aiki tare a bangarori daban-daban da suka shafi kur’ani mai tsarki.
Haka nan kuma yarjejeniyar ta shafi shirya gasar kur’ani waddaza ta hada bangarorin biyu, inda za su gudanar da ayyuka na hadin gwiwa a wannan fage a cikin kasashensu.
Babbar manufar hakan dai ita ce kara yada lamarin kur’ani a cikin al’ummomin kasashen biyu, musamman ma matasa masu tasowa a wanann lokaci, wadanda suke bukatar tarbiya irin ta kur’ani mai tsarki.