Tashar talabijin ta Almasirah ta bayar da rahoto daga birnin San’a fadar mulkin kasar Yemen cewa, a daren jiya mayakan haya na gwamnatin Saudiyay sun harba makaman atilare a kan kauyen Al-rabsa da ke cikin gundumar Hudaida, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mata biyu da kuma jikkatar wasu.
Wadannan hare-haren dai na zuwa kokarin da Saudiyya take yi tare da taimakon Amurka da wasu kasashen turai, domin mamaye lardin Al-hudaida mai matukar muhimamnci a kasar Yemen.
Ko a ranar Lahadin da ta gabata Saudiyya ta kashe fararen hula a cikin kauyukan Shajin, Al-Munqim da kuma Duraihami da ke cikin gundumar ta Al-hudaidai a yammacin kasar Yemen.
3926575
Kekuma