IQNA

Jam’iyyar Alwifaq Ta Bahrain Ba Ta Goyon Bayan Kulla Huldar kasar Da Isra’ila

22:38 - October 19, 2020
Lambar Labari: 3485289
Tehran (IQNA) babbar jam’iyyar siyasa a kasar Bahrain ta yi watsi da shirin gwamnatin na kasar na kulla hulda da gwamnatin yahudawan Isra’ila.

Wannan na zuwa ne a wata sanarwa da jam’iyyar ta “Alwifaq” ta fitar inda  ta bayyana cewa; A ranar Lahadi sha takwas ga watan Oktoban wannan shekara tawagar ‘yan sahayoniya ta isa Bahrain a daidai lokacin da al’ummar suke cike da fushi, kuma mahukuntan kasar sun dauki tsauraran matakai na tsaro.

Bugu da kari sanarwar ta ci gaba da cewa; Mahukuntan kasar sun yi amfani da ‘yan bada domin hana al’ummar kasar bayyana fushinsu akan kulla alaka da ‘yan sahayoniyar.

Jam’iyyar ta “Alwifaq’ ta kara da cewa; Alakar da mahukuntan kasar su ka kulla da ‘yan sahayoniya ta sabawa doka, domin ba ta wakiltar al’ummar kasar da basu yarda da ‘yan sahayoniya barayin kasa ba.

Wani sashe na sanarwar ya kunshi cewa; Tabbas al’ummar kasar ta Bahrain za su ga bayan wannan haramtacciyar yarjejeniyar da ‘yan sahayoniya.

3929977

 

captcha