IQNA

Shugaban Jibouti Bai Amince Da Matakin Wasu Kasashen Larabawa Na Kulla Alaka Da Isra’ila Ba

22:52 - December 24, 2020
Lambar Labari: 3485488
Shugaban kasar Jibouti ya bayyana rashin amincewarsa da matakin da wasu kasashen larabawa suka dauka na kulla alaka da Isra’ila.

A zantawarsa da tashar talabijin ta Aljazeera, shugaban kasar Jibouti Isma’il Umar Guella ya bayyana cewa, wasu daga cikin kasashen larabawa sun kulla alaka da Isra’ila bisa hujjar yarjejeniyar da kasashen larabawa suka cimmawa kan hakan.

Ya ce wadannan kasashe sun sabawa wannan yarjejeniya, wadda tsohohon sarkin Saudiyya marigayi sarki Abdallah ya gabatar da ita, wadda ta kunshi cewa, idan aka kafa kasashe biyu wato Falastinu da Isra’ila, kowace mai cin gishin kanta, to a lokacin Larabawa za su iya amincewa da Isra’ila  a matsayin kasa.

Shugaban na Jibouti ya ce babu ko daya daga cikin wadannan sharudda da suka tabbata, a kan haka babu dalilin fakewa da sunan yarjejeiyar larabawa wajen kulla hulda da gwamnatin yahudawan Isra’ila,a  lokacin da take mamaye da Falastinu.

Haka nan kuma ya bayyana rashin amincewarsa da hankoron wasu na mayar da tashoshin jiragen ruwa na yankin a mjatsayin warare na aiwatar da siyasa, maimakon harkoki na kasuwanci da tattalin arziki.

3943058

 

 

 

captcha